Fati Washa wadda aka fi sani da Fatima Abdullahi Washa, tana ɗaya daga cikin fitattun jaruman Kannywood, wato masana'antar shirya fina-finai ta Hausa da ke Arewacin Najeriya. An haife ta a garin Bauchi kuma ta shahara saboda rawar da take takawa a fina-finan Hausa tun lokacin da ta fara fitowa a cikin wannan masana'anta. Fati, ta fara fitowa a cikin fina-finai da dama, tare da shahararrun jarumai na Kannywood, inda ta samu daukaka saboda kwarewar ta a fagen wasan kwaikwayo.
Zantuka
edit- ina jin daɗi idan naga masoya na musamman a lokacin da suke nuna farin cikinsu na gani na da suka yi.
- rayuwa bata da sauƙi ,amma dole ne mu ci-gaba da yin gwagwarmaya ,yadda komai wahala Mutum ya ci-gaba da jajir cewa .
- Ba zan bari komai ya karya min zuciya ta ba komai tsakani.
- Duniya makaranta ce kowa na koyan darasin da ya dace da shi.
a